Thursday, February 24, 2011

BABA DA 'YAN DIYA


BABA DA ‘YAN [IYA

Yana da wahala wanda ya ]an]ani za}in sana’ar Adabi ya halarci Kasuwar Ukazan da ke ci a Kwalejin Abubakar Gumi duk }arshen zangon karatu na farko ba ta burge shi ba

[alibai da Malamai wa]anda Allah yai wa baiwar wa}a sukan baje kolinsu da wa}o}i a kasuwar.

Wannan wa}a tana daga cikin abubuwan da kasuwar ta haifar a shekarar karatu ta 2004/05.

A lokacin nine nake matsayin baban aji ]aya ‘A’ na }aramar sakadare. Sai na ga dacewar in ]an wa}e ‘yan yaran, saboda la’akari da cewa akwai wasu ubannin azuzuwan da su ma sun yi wa azuzuwansu wa}a.

Karin wa}ar iri ]aya ne da na wa}ar Danniya



Ga wa}ar:

1.    ’Yan One A da ku nake
             Yaran gaskiya

2.    ’Yan kirki na ke kira
             Amsa bai ]aya

3.    Yara masu laddabi
            Don ba sa tsiya

4.    Ba sa latti don haka
            Ba sa shan wuya

5.    Sun gane karatuka
            Babu da}i}iya

6.    Yara masu kwalliya
            Babu }azamiya

7.    Gun kyau ba kamar ya su
            Ko zinariya

8.    Har mamanku Raudatu
            Ka ji masoyiya

9.    Na gaishe ki na yaba
            Nai maki godiya

10.  Yarana ku ]an tsaya
            Zan muku tambaya

11.   Waye za ya ja da ku?
             Ba shi a Kulliya

12.   ’Yan One B ina suke?
             Ba su da zuciya

13.   ’Yan One C fa ya suke?
             Ka ji gidan wuya

14.    Ku One D ku ba ni gu
             Ba ku da zuciya

15.    ’Ya’yana abin yabo
             Su duka bai ]aya

16.    Ga ladabi da hankali
             Ga su da juriya

17.    Allah ba su illimi
             Ya Sarki ]aya

18.    Imani da]a masu
             Sun zama auliya

19.   Aljanna ka sa su je
             Can Firdausiya

20.   Gun aure ka sa su samu
             Marasa tsiya

21.   Ba duka da tsangwama
             Ba kuma shan wuya

22.   ’Yan One A da Asgari
             Baba da ‘yan ]iya

23.   Ma’assalam da ku nake
            Yaran gaskiya

30 ga watan Disemba, 2004.

Zariya.

BABA DA 'YAN DIYA


BABA DA ‘YAN [IYA

Yana da wahala wanda ya ]an]ani za}in sana’ar Adabi ya halarci Kasuwar Ukazan da ke ci a Kwalejin Abubakar Gumi duk }arshen zangon karatu na farko ba ta burge shi ba

[alibai da Malamai wa]anda Allah yai wa baiwar wa}a sukan baje kolinsu da wa}o}i a kasuwar.

Wannan wa}a tana daga cikin abubuwan da kasuwar ta haifar a shekarar karatu ta 2004/05.

A lokacin nine nake matsayin baban aji ]aya ‘A’ na }aramar sakadare. Sai na ga dacewar in ]an wa}e ‘yan yaran, saboda la’akari da cewa akwai wasu ubannin azuzuwan da su ma sun yi wa azuzuwansu wa}a.

Karin wa}ar iri ]aya ne da na wa}ar Danniya



Ga wa}ar:

1.    ’Yan One A da ku nake
             Yaran gaskiya

2.    ’Yan kirki na ke kira
             Amsa bai ]aya

3.    Yara masu laddabi
            Don ba sa tsiya

4.    Ba sa latti don haka
            Ba sa shan wuya

5.    Sun gane karatuka
            Babu da}i}iya

6.    Yara masu kwalliya
            Babu }azamiya

7.    Gun kyau ba kamar ya su
            Ko zinariya

8.    Har mamanku Raudatu
            Ka ji masoyiya

9.    Na gaishe ki na yaba
            Nai maki godiya

10.  Yarana ku ]an tsaya
            Zan muku tambaya

11.   Waye za ya ja da ku?
             Ba shi a Kulliya

12.   ’Yan One B ina suke?
             Ba su da zuciya

13.   ’Yan One C fa ya suke?
             Ka ji gidan wuya

14.    Ku One D ku ba ni gu
             Ba ku da zuciya

15.    ’Ya’yana abin yabo
             Su duka bai ]aya

16.    Ga ladabi da hankali
             Ga su da juriya

17.    Allah ba su illimi
             Ya Sarki ]aya

18.    Imani da]a masu
             Sun zama auliya

19.   Aljanna ka sa su je
             Can Firdausiya

20.   Gun aure ka sa su samu
             Marasa tsiya

21.   Ba duka da tsangwama
             Ba kuma shan wuya

22.   ’Yan One A da Asgari
             Baba da ‘yan ]iya

23.   Ma’assalam da ku nake
            Yaran gaskiya

30 ga watan Disemba, 2004.

Zariya.

Thursday, February 17, 2011

Danniya

DANNIYA
 
Khadija AbdulLahi Usman suna ne da ba zai yiwu in manta da shi da wuri ba.
Wata yarinya ce da aka ta~a sa mani ranar aure da ita! Sai da abubuwa da shirye-shirye suka kankama, sai mahaifinta ya ce ba zai yiwu ba, bisa dalilin rashin fahimta tsakanin shi da wasu ‘yan uwansa sa }auye kamar yadda ya ce, sakamakon haka komai ya wargaje.

Duk da yake ba wai na damu ne fiye da }ima ba, amma na ga dacewar in sajjala abin da ya faru a wa}e, don tarihi da kuma biyan bu}atar zuciyata ta adabi.

Wa}ar tana da layi bibbiyu ne. Karinta na wa}ar baka ne. Kuma na same shi ne daga wani fim din Hausa mai suna {ugiya. Duk da yake har zuwa yanzu da nake rubuta wa]annan bayanan ban kalli fim din ba! Ina dai jin wa}ar ne kawai a bakin yara da mata.

Ga wa}ar:

1.    Na gode wa Rabbana
Sarki ne ]aya

2.    Na yi yabo da gaisuwa
            Tun daga zuciya

3.    Gun baba ga Fatima
            Khairul Anbiya

4.    {unci ya yi dandazo
            Ya cika zuciya

5.    An zalunci mai ita
            An masa danniya

6.    Manya sun yi yaudara
            Sun yi halin tsiya

7.    Bayan sun yi rantsuwa
            Alkawari ]aya

8.    Sun karya shi kai tsaye
            Sun }i su tausaya

9.    Allah Rabbi ya sani
Ba su da gaskiya

10.   Hujja wacce za su ban
            Sun rasa ko ]aya

11.   Sai dai kame-kame
            Sun ma ban dariya

12.   Dije ]iyarka ce na’am
            Sai dai ]an tsaya

13.   Zan maka ]an tuni a nan
            Don ka rage tsiya

14.   Aure gun ta dole ne
            Komai zilliya

15.   Duk da kana ganin kamar
            Kai mani danniya.   

16.  Ai wani za ka bai ita
            Ko da ka }iya


17.  Komai son ta ba ka
            Aure wannan ]iya

18.  Dole ka ba waninka
            Har yai mata kishiya

19.  Kuka na ina ta yi
            Gun Allah ]aya

20.  Allah ya isa na yi
            Sam ba yafiya

21.  Ka zalunci rayuwar
            Dijale ‘yar ]iya

22.  Ka raba so na gaskiya
            Ka yi abin tsiya

23.  Ka hana ‘yarka yin
            Karatu don }aniya

24.  Ka sanya ta ta yi fail
            Allah wadan tsiya


25.  Tir da uba irin ya kai
            Ya mara zuciya

26.  Wanda kwa]ai ya haukata
            Mai wautar tsiya

27.  Dije ki han}ure kawai
            Kad da ki dulmiya

28.  Ba ki da hope wurin uba
            Don bai gaskiya

29.  An }wacen ki jarumi
            An miki danniya

30.  Na rufe baitukan anan
            Don ban son tsiya

23 ga watan Agusta, 2005.

Zariya