TUWON GANDU
A watan Agusta na shekarar 1997 na kammala karatuna na Difuloma a Misau. Lokacin ne na rubuta wannnan wa}a. Na yi ta ne da nufin zaburar da matasa akan su tashi su yi karatu. Saboda a lokacin na lura da cewa matasanmu ba wai suna wani son karatu ne ba. Mafi yawa suna kwana ne su tashi da burin su yi ku]i dare ]aya ba tare da sun yi wata wahala ba.

Wa}ar mai }war hu]u ce, don haka take da ]angon ciki da na waje kamar yadda mai karatu zai gani.

Karinta na wa}ar baka ne, tana da amshi kamar haka:
           
Neman ilimi a yanzu shi ne ja baya
Don haka arzikinmu kullum ba ya nuna.

Sunan wa}ar Tuwon Gandu. Na sa mata wannan sunan ne saboda la’akari da cewa kowa na bu}atar ya yi amfani da abin da ta ke karantarwa kamar yadda ya ke bu}atar tuwon gandu.

Ga wa}ar nan:

1.         Allah ya Tabara kai ne Babban Sarki
            Ro}ona gareka Allah ni zan ]auki
            Al}alami in zana wa}a domin ]oki
            Ka ban fasaha Allah in cika burina

2.         Allah Rabbi kar ka sa in yi halin jaki
            Ka ban fasaha, ilimi har da yawan baki
            Ka kare sharri a garan ya Allah Sarki
            Ka bani kaifin lura ya kar Maulana

3.         Allah salli ya Ilahi gun manzona
            Alayensa har sahabbai gun mai suna
            Ahmadu ]an Amina zainun nurun fina
            Har matansa sayyadi ]a ne ga Amina

4.      Wasu ‘yan baituka nake son yi don na kira
            Yara ‘yan uwa musulmai sai a yi lura
            Kan ilimi nake nufin ni zan yi batuna
            Duk mu zage mu nemi hanyarmu ta Aljanna




5.         Kar ki yi wauta ki gane jigon zancena
         Kalmar ilimi na ke wa campain a ganina
         Ba wata tsada gare ki ke ‘yar babana
            Sai dai ilimi ina fa]a maki Auntiena!

6.      Kai ma ]an samari zancena na kanka
            Ba daraja gareka sai ka san dininka
            Ka san Rabbana da tarihin Manzonka
            Sannan sai ka nemi hanyar nan Aljanna

7.         Girman kanka jingine kar ka bi ‘yan baya
            [au allonka ko takardunka ka ]au hanya
            Je gun malami ka ce masa “Na zo koya”
            Kar ka yi wasa wata ran kai ma ka nuna

8.         In ya biya ma ka ro}i Allah ka yi bita
            Ka zage damtse kar ka bi hanyar ‘yan mata
            Kar ka sake a bar ka can baya kana wauta
            {arshe ma ka zam kamar ~era kaicona

9.         Ke ma ‘yar uwa ina fayyace sa}ona
            Gare ki, zancen ilimi shi ne burina
            Kar ki biye ta mai yawan shirme mummuna
            In kuwa kin }i ji ko kin tabbata dai sauna

10.       Talla zuwanki ]akunan gayu shirme ne
            Gulma da yin acha~a aikin matsiyata ne
            In kuwa kin }i sai mu ce wannan ai cus ne
            Ba ki da martaba idon mu da ke sai zana

11.       Saurara in ba ki haske ke yarinya
            Ai daraja tana ga mai ilimi, tarbiyya
            Ba wai sa skirt da anko ba da yin }arya         
            Ba kuma bin maza da talla ba har can gona

12.       In ma ban da sakarai mai wauta ke ma
            Ba ki ganin samarunkan ko da sun nema
            In sun gane jahila ce sai su ji }yama
            Waye za ya saura sai dai wawa sauna

13.       Ilimi garkuwa ta ya}in neman hanya
            Ta zuwa Jannatun-na’im ka ji wurin hayya
            Tashi ka nemi garkuwa kar ka ji ‘yar kunya
            In ka sake ko ba ruwana ko oho na

14.       Zan maka tambaya ka amsa in za ka iya
            Ka ta~a cin karo da mai ilimi na baya?
            Ko kuwa bai da martaba ko kuma ya kaya?
            Amsa mana in ka na da amsar mutumina

15.       Abin da zan ce maka har ke ma ‘yar gata
            {arshe ko in ce da ku babbar manufata
            In nushe ku martabar ilimi da nagarta
            Addininmu sai da ilmi ya dangina

16.       Boko ma muna bu}atar mu karanta shi
            Musulunci da shi gaba ]ai mu nazarce shi
            Nau’in ilimi ko wanne mu ka kalato shi
            Ka sanya addini a gabanka abokina

17.       Duk wani ~angare na ilmi babu na baya
            Ko wanne ka sami damar shi ka ]au hanya
            Kai dai kar ka zam kana layin ‘yan baya
            Sune jahilai da kullum ba sa nuna

18.       Mu jona ilmin mu da manyar makarantunmu
            Har ma jami’a idan dai har mun samu
            Amma sai mu gyara hali da ]abi’unmu
            Halayenmu yau matasa sai an zauna

19.       Abin takaici yanzun duk makarantunmu
            Da jami’o’i da cibiyoyin iliminmu
            Sun zama centres a nan muke ~ata halinmu
            Holewa kawai matasanmu suke }auna

20.       Wannan shi ya sa a kullum ba sa lura
            Ba bitar karatuka kullum sai fira
            Sai satar da in dubu tac cika sai kora
            Don Allah mu gyara halaye dangina

21.       Duk wani shirme ka bar shi ke ma sister ta
            Ku ]au batun nan ilimi hanya ta nagarta
            Ka bar Husaina ko kuma je ka ka aure ta
            Ke kuma }yale ]an samari ya ji zancena

22.       Shinkun nan ba}a da kin ka saka a gabanki
            Ba daraja ba ce abin kunya ce gun ki
            Kai ma mai biye ta za kui kunnen-doki
            Sai an ba ka withdrawn ka gane batuna

23.       Ka lalata rayuwar yarinya kai ma
            Ka watsar da naka ilmin da ka zo nema
            Ka zamto abin kwatance, kuma an sa ma
            Suna wai ana fa]in gwarzo na Husaina

24.       Kin tozarta ‘yan uwa, dangi, babanki
            Wanda ya yarda ke rashida ce yab bar ki
            Kin ka taho wurin karatu amma kin }i
            Sai shirme ki ke kina aiki mummuna

25.       Ban ce kar ku nemi aure ba abokaina
            Ku janye zargin ku a kai na sisters ]ina
            Ba wai na hana ku soyayya ba batuna
            Amma so irin na shirme shi nan nuna

26.       In kuwa kun ga kun amince aure za kui
            Kun kuma yarda babu shunku ba}a to sai kui
            Soyayyarku, har ku cim ma buri har kui
            Adu’a, Rabbi taimaka mana ya Maulana

27.       Ba zagin ka nai ba sarki na gidan yamma
            In ka lura duk nasiha ce da nake ma
            Addininmu ko nasiha ne can dama
            Duk wani huci da ka ke don Allah ka daina

28.       Ke ma malama idan dai har kin lura
            Na san za ki gane zancen ban da harara
            Wata}il da kina jira ne sai na rera
            Ki ce da ni zancen banza kai ne sauna

29.       Kan zabon da angulun nan ta saka shi ma
            Kifi na ganin ka ya kai  mai jan koma
            Gara ka bar halinka in ka }i ko to kai ma
            Ka ta~e ka kauce layi ka zamo sauna

30.       Ba wai na fi duk mutane baki ne ba
            Ba kuma na fi duk na zaune karatu ne ba
            Ba ilimi  garan ba, ban ce ban nema ba
            A ‘a sai yawan karambani aikina

31.       Duk zancen da naf fa]a ba sabo ne ba
            Sai dai tuntuni da kullum bai }are ba
            Kan wannan batu na ilmi ban fasa ba
            Hanyar tsira Ubangiji Allah nuna

32.       Wa}an nan a nan nake son na takaita ta
            Allah kai min dacewa kan manufata
            Allah sa mu gane zancen da na yo bita
            Ban ilimi Tabara Sarki Mahaliccina

34.       Sunana Kabir, a Zariya nai wayona
            Ba na tantama dukanku kuna da sani na
            Wa}an nan da nay yi ranar goma na zana
            Ga watan Yuli, Rabbana sa na ga manzona
           
10 ga watan Yuli, 1997

Misau.