Tuesday, November 30, 2010

KAFIN MU JE DA NISA


KAFIN MU JE DA NISA

Na da]e ina rubuta wa}o}i iri-iri, akan abubuwa dabam-dabam. Duk da yake yana da ]an wuya in iya tuno wa}ar da na fara yi. Musamman saboda akwai wasu wa}o}ina da suka ~ata. Zan dai iya tuna cewa lokacin ina aji biyu na babbar sakandaren Larabci ta Jama’atu da ke Zariya, Malam Ma}ari Sa’id, wanda shi ne shugaban makarantar a lokacin, ya koya mana Arulin Larabci. Yai ta kwa]aitar damu mu dinga }o}arin tsara wa}a, wannan ya taimaka mini }warai wajen gane cewa ina da baiwar rubuta wa}a.

Yana da kyau na ambaci cewa a farko-farkon al’amari na fara yin wa}o}ina ne da harshen Larabci, amma daga baya sai na ji na fi son rubuta su da harshen Hausa, saboda wasu dalilai, daga ciki akwai kasancewar Hausa yarena na asali. Ko ba komai, na fi iya sarrafa shi fiye da duk wani harshe.

Baya ga haka mutanen da nake sa ran su karanta wa}e-wa}ena a karo na farko sune Hausawa. Har ila yau ina ]aukar wa]annan wa}o}i a matsayin wata ‘yar gudummowa tawa ga ci gaban Adabin Hausa. Wannan ya sa na ke fatar kundin wa}o}in ya yi tsawon rai da farin jinin da zai sanya manazarta Adabin Hausa su waiwaye shi.

Wa]annan da ma wasu dalilai suka sanya ni rubuta wa}o}i da dama cikin harshen Hausa.

A wannan kundin zan yi }o}arin tattara wa]anda Allah Ma]aukakin Sarki ya ba ni ikon tattarawa ne kawai. Zan kuma ]ebo mafi yawan su ne daga asalin rubutun hannun da na yi na wa}o}in.

Zan yi }o}arin zayyana dalilin da ya sa na rubuta kowace wa}a kafin in kawo mataninta. Tare da fa]in ma’auninta da dai duk wani bayani da na ga dacewar kawo shi a matsayin shimfi]a ga wa}ar in Allah ya so.

Yana da kyau a nan na ambaci cewa duk wa}o}in dake cikin kundin nan nawa ne na kaina. Inda kuwa ya zama akwai hannun wani to zan ambata, kamar wa}ar Tsuliyar Dodo, a cikin ta  akwai baitoci da dama wadanda suke gudumowa ce daga ]an uwa Muhammad Nura Yahaya.

Sai kuma kare-karen wa}o}in wa]anda mafi yawansu na samo su ne daga wasu wa}o}i da na ji ko na karanta. Wannan kuwa ni a ra’ayina ba satar fasaha ba ne ba kuma laifi ba ne, don shi kari na kowa ne in dai yana da abin da zai fa]i da shi. A gani na kari kamar yare ne; wanda wani bai isa ya hana wani magana
 da shi ba, abin nema kawai a ce kana jin yaren yadda ya kamata ka iya magana da shi.

Don haka nake ganin cewa kare-karen wa}o}in da na ]auko daga wasu wa}o}i  na wasu mawa}a ba satar fasaharsu bane, ko ba komai su ma ko kuma in ce wasu daga cikinsu ]auko su suka yi daga wasu wa}o}in na wasu mawa}an dabam. Don haka nai ta bayyana inda na samo kowane kari a inda ya dace in bayyana hakan

Ba na cewa zan jero su a kan wani tsari na musamman. Zan kawo su ne kawai yadda na samu dama, ba wai don kasala ko rashin tsari ba, sai don }arancin lokaci da rashin sukuni.

Ko da wasa ba na jin cewa aikina kammalalle ne, don haka kamar ko wane aiki a fagen Adabi, wannan kundi karan bara ne ga masana, malamai da masu nazarin Adabi.
Fatana su yi ma wa}o}in nazari da na}adin da zai taimaka wajen gyara kurakurena, }ayata wa}o}in fiye da yadda suke a yanzu da taimaka wa masu karatu }ara fahimtarsu. Da hakan ya zama wani aiki da zan kasance mutum na farko da zai yi farin ciki da shi.

Ina neman taimakon Allah nake cewa a sha karatu da nazari lafiya.
                             
Kabir Abubakar Al-Asgar

25 ga watan Satumba, 2006

Zariya.

No comments:

Post a Comment