Wednesday, January 5, 2011

BAKANDAMITAR KULLIYYA

BAKANDAMIYAR KULLIYA

Wani lokaci can baya a watan Yuli na shekara ta 2002 ina zaune a gida da yamma, zan iya cewa ina hutawa ne ko kuma ina kokarin murmurewa daga wani zazza~i da bai da]e da saki na ba. Sai na ga dacewar in yi wa malamai abokan aikina a Kwalejin Abukar Gumi wa}a. Na yi haka ne da nufin wa}ar ta zama wani kundi na bayanai da zan iya amfani da shi wajen tuno su ko bada]e ko bajima.

Nan take sai na dauki biro da takarda na fara rubuta wa}ar wadda na }arasa ta bayan sallar isha ta wannan ranar. Sannan na rera ta a Kasuwar Ukaza wacce nai bayani a can baya cewa tana ci duk shekara a Kwalejin.

Wa}ar kwar hudu ce, tana da karin Larabci ne da ake ce masa Wafir. Sunanta ko kamar yadda ka karanta a farko “Bakandamiyar Kulliya

Ga wa}ar:

1.   Da sunan Rabbi wa}a za na fara
      Ina ro}o gare Shi ya ban basira
      Da]an hikima Alimu ka bani lura
      In tsara yabon da zan yi wa ‘yan uwana

2.   Ina da]a sallama kuma nai salati
      Ga manzona uba gun Binta Fati
      Da manyan masu tsarki Alu-Baiti
      Inai muku gaisuwa a cikin batuna

3.   Sahabbai ku gaba ]aya na yabe ku
      Ha}i}a babu wanda ya kai kamarku
      Rasulu kuke wa ]a’a babu shakku
      A Makka da sanda yay yi zama Madina

4.    A yau wa}ar ga Higher zana yi ta
       In bayyana martabar ta in karrama ta
       Ku bi ni a hankali duk za na furta
       A wa}an nan da zan yi wa malamaina 

5.    Higher Islam ta Zariya sayyida ce
       Gidan ilimi, ha}i}a ta kasance
       Uwa mai ba da mama ha]a]]iya ce
       Gaba ]aya ba kamar ta jihar Kaduna

6.    Karatu ~angaren boko akwai shi
       Na addini ko nan ne dandalin shi
       Dukan fanni na ilmi to akwai shi
       Bila shakkin nake saito batuna

7.    A Higher za a koya ma karatu
       A}ida, har da Kur’ani ka saitu
       Ka waye kanka ba ya cikin akwatu
       Dukan ilimi ka san shi ka zarce sauna

8.    Kimiyya har da lissafi akwai su
       Da Larabci da Turanci ka ji su
       Ka zamto malami ka }ware a darsu
       Ka zarce sa’a da sauran alamina

9.    Ina teachers na Higher kun yi kirki
       Kuna koyar da yara babu birki
       Inai muku sannu na yaba wanga aiki
       Rahimu ya sanya sakamakon ku Janna

10.   Aliyyu Principal ai jarumi ne
        Wajen ilimi da kamewa gwani ne
        Tafarkin ayyukan shi abin yabo ne
        Rahimun Rabbi kare malamina

11.   Cikin zamaninka ne Higher ta farka
        Ta ]aukaka har ta zarce sa’a a harka    
        Gaba ]aya ci gabanta yana gareka
        Ha}i}a na yaba ma shugabana

12.   Aliyyu Rufa’i kai ma na kira ka
        Inai ma jinjina kuma na yabe ka
        A mulkin duk da kai ba ma da shakka
        A kan ka kama hanyar adilina

13.   Hakan nan Vice imam ne, zahidi ne
        Yana da yawan sani, kuma kamili ne
        Abin koyi, wajen fi}ihu gwani ne
        Ba zan manta da kai ba cikin batuna

14.   Rabo ]an Abdu Musa ya yi aiki
        Wajen ]a’a, yana da hali na kirki
        Yana da yawan kula, kuma bai da raki
        Gwanin kyauta da karrama malamaina

15.   Ina ]an Shisu ango ne ga Fati!
        Wajen Adabi yana bayar da baiti
        Bi fadlika kan Adab an sami saiti
        Kabiru yana yaba maka ]an uwana

16.   Basiru Abu-Habiba ina yabon ka
        Wajen iya furta sauti ba kamarka
        Gwani ne kai kana cika ayyukanka
        Ilahi ya taimaka maka jarumina

17.    Jawabi ka iya shi }warai Haruna
         Wajen hikima da hujja ka fi sauna
         Wajen aikinka ba wasa Haruna
         Ina fatan musun nan za ka daina!

18.    Fari mai kyan hali AbdulMaliki
         Wajen Nahawu ha}i}a ka yi aiki
         Hakannan ba ka yin rowa ga maki
         Yana da halin tawali’u jarumina

19.    Habawa Alhajin Allah Jamilu!
         A Mathematics fa dole a sa Jamilu
         Ina rokon Ilahi Zul Jalalu
         Ya ma baiwa ta aure sahibina

20.    Uba ga Nusaiba KB malamina
         Inai maka jinjina ya sayyadina
         {ira’an nan da kak ke kar ka daina
         Ilahi ka ninka ladan ]an uwana

21.    Imamu Sa’id ina kai gaisuwata
         Uba ne kai wajen yara da mata
         Mutum ne kamili kuma bai da mita
         Allahu ya kare gwarzon malamina

22.    Muniru Abubakar na zo gare ka
         Inai ma jinjina don ba kamarka
         Kana bun}asa ilmi ba ruwanka
         Da wawayen mutane zalimina

23.    Habu Sabo mutum ne mutunci
         Da kamewa, sa’annan ga kawaici
         Akwai ha}uri wajen sa da salihanci
         Inai ma jinjina ya ]an uwana

24.    Uban Jummai da Mathematics Zubairu!
         Shahadar Maths inai maka ni Kabiru
         Professor kake gun Maths Zubairu
         A fannin babu tsara gun gwanina

25.    Iyayen ka’ida Malam Habibu!
         Tsakanina da shi kun san da hubbu
         Allahu ya taimaka maka ya Habibu
         Bisa tsare ayyuka don kar ka daina

26.    Tazarce Rabi’u, gwarzo a Higher
         Akwai shi da kwarjini ba ya musayya
         Lawal Garba ina gaishe ka lauya
         Allahu ya sa ka zam gwamnan Kaduna!

27.    Mutan birni su Salisu na kira ku
         Wajen Business a Higher na kamarku
         Ka sai da tufa ka koyar babu shakku
         Allahu ya ba ka dacewa batuna

28.    Hasan Sabo uba ne shi na kowa
         Yana bayar da ha}}i bai da rowa
         Primary tashi ce kowa da kowa
         A gai da Hasan uba gun ]alibaina

29.    Da malam Amadi mai Hausa sannu
         Akan aikinka ba ka }yale dainu
         Ina gaishe ka sannan na yi sannu
         Tabaraka Rabbi kare jarumina

30.    Kabir M.K. da Gboko ina yabonku
         Da Yusufu Imtihani ]an uwanku
         Aliyyu da Sani na dawo gareku
         Primary taku ce ya ‘yan uwana

31.    Da malam Nasirunku da Jafaruna
         Da Auwal Sani shi ne malamina
         Da shi da Aliyyu babban sahibina
         Inai maku sallama ya malamaina

32.    DhiyaudDini na dawo gareka
         A safe da yamma ba gwarzo kamarka
         Wajen aiki da bayyana mazhabinka
         Ka saurara gareka nake batuna

33.    Umar Sheshi Kabiru yana kiranka
         Da kai da Umar Abas ai babu shakka
         Kuna tsayuwa akan aikin da harka
         Kuna daga martabar Higher wurina

34.    Bashiru Lawal fitaccen malami ne
         A fannin Arabiyya hazi}i ne
         A boko ya wuce raini ku gane
         Ya Rabbi ka }ara ilmi gun gwanina

35.    Ina Ironmu [an Asabe gwanina
         Mutum ne kamili kuma bai hiyana
         Yana cika ayyuka da tsare amana
         Sakin fuska ]abi’ar malamina

36.    Lawal ango na Hauwa da na kira ka
         Ka amsa kai da Hauwa uwargidanka
         Da kai da ita kuna ]aga wagga harka
         Ta Higher Allah saka malamaina

37.    Lawal sarki na teachers sai gareka
         Ina kake malamin Higher in gan ka
         Kana koyar da tafsiri da kanka
         A da can ya akai yanzun ka daina?

38.    Bala ]an Bauchi ne ai ]an garinmu
         A don haka koda yaushe kuke ganin mu
         Muna yin fira labarin jiharmu
         Ta Bauchi }asar da can ne assalina

39.    Haba M.A. ka saurara ka ji ni
         Ka tabbata ka fi raini ni gare ni
         Gama kai ne fa Master yau gare ni
         Ina fatan ka dara kan batuna

40.    Da Malam Abdu kai ne walfayanmu
         Kana kuma nuna jin tausai garemu
         Kana samar da hallin mushkilarmu
         Ina rokon Ilahi ya }ara }auna

41.    Da NuridDini Exams Officer ne
         Ina ]an Bello Shehu abin yabo ne
         Dama AbdulAzizi mujahidi ne
         Ina gaishe ku ya ku malamaina

42.    Habun Shika har Sulaimanu gare ku
         Da Hamza Abas da sauran ‘yan uwanku
         Primary ku ku ke gyara da taku
         Kuna aikin a-zo-a-gani wajena

43.    Ina kake ya Namata ina kiran ka
         Da Shisu da Mustafa Allah ya saka
         Da Hamzatu malami ne babu shakka
         Inai muku jinjina ya malamaina

44.    Mutanen nawa kun ga yawa garesu
         A don haka bai yiwo na }ididdige su
         Wa]ansu da }yar fa in ma zan tuno su
         Ku min uzuri ku yafe kuraraina

45.    Ku min afuwa wa]anda na tsallake ku
         Gazawa ce da rauni gun }aninku
         Ku yafe, }addara ce ta fa auku
         Allahu ya sa ku gane dukan batuna

46.    Ina ro}on Ilahi ya }ara himma
         Ga dangina ya ba su sifa ta girma
         Su zarce sa’a su kere dukka tsama
         Ya }yautata ayyukansu ga ]alibaina

47.    A nan zan dakata domin na huta
         Da wa}an nan da tun tuni nai ta bita
         Bakandamiya ta Higher nak kira ta
         A dandamalin Ukaza nake batuna

48.    Kabir, kun san ni ba ba}o bane ni
         A wa}ar Hausa ba sabo bane ni
         A da can na yi nan gaba za ku ji ni
         Da ikon Rabbi Sarki Khalikina

49.    Inai muku sallama dangi ku amsa
         Abin da kuke na kirki kar ku fasa
         A nan zan ]an tsaya domin na nisa
         In ce Allah ya saka malamaina

27 ga watan Yuli, 2002
  
Zariya.  


1 comment:

  1. How to play Baccarat on the online casino
    Baccarat is an ancient card game which is played at the 바카라 사이트 카지노 판 village of Yucatan. It was the first to become available in the United States for two

    ReplyDelete