Thursday, January 13, 2011

DARUL HADITH

Na yi hidimar }asa wayo a shekarar 2005 a garin Abeokuta, babban birnin jihar Ogun. A lokacin da na zo tafiya sansanin matasa masu yi wa }asa hidima a Shagamu, sai na ga dacewar na yi wa wasu ]alibaina na makarantar Darul Hadith bankwana na musamman a wa}e. Don haka ‘yan kwanaki kafin na bar Zariya zuwa Shagamu sai nu rubuta wannan wa}ar.

Wa}a ce mai kwar hudu. Karinta ina tsammanin asalin shi na wa}ar ga]a ne. Amma ni dai na ]auko shi ne daga wakar ]an uwa Malam Adam Abul-Abbas wadda ya yi mai suna Hijabi.

Ga wa}ar:

1.    Darul Hadisi ina son ki
       Da ke da duk ma’abotanki
       Ina nufin ]alibbbanki
       Gare su nai shaidar kirki

2.    Darul Hadisi gidan Sunna
       Ajin da ya zarce ko ina
       Ga ]alibai marasa sakana
       Wa]anda raina ke }auna

3.    Mun yi karatoci da yawa
       Littattafai har saukewa
       Duk Juma’a ba fasawa
       Karatuka muka bayarwa

4.    A da mu kan yi da an sauko
       A juma’r kowane mako
       A yanzu ko loton farko
       Na safiyar Juma’ar mako

5.    Mun ka karanta [ahawiyya
       Wurin a}idar salafiyya
       Mun sauke Allah ya biya
       Ya ba mu iko na biyayya

6.    Da Tabsira mun sauke ta
       Ka sanya Umda bayanta
       Sanya Adab sai ka dakata
       Akwai ragowa zan furta

7.    Ina nufin Talkhisin nan
       Na Siffantun malam din nan
       Albani ta hadisan nan
       Da ma Janaza kuma san nan

8.    Mun ka yi littafin Nahawu
       Da Sarfu kui ta biyar sawu
       Na baitukan in nai sahawu
       Ku ]an tuna mani kui afwu

9.    Da Musdalah mun koye shi
       Shi da Usul don mun yi shi
       Dukan su komai da ka ji shi
       Dalla-dalla ba }unshi

10.  Ya ]alibai gani gareku
       Ina yabawa dukaninku
       Don kuwa in dai da ba ku
       To ai ba makarantarku

11.  Kuna ta jure zuwa darasi
       Ko da ba ku da ko sisi
       Allah ya sa ranar ba’asi
       Mu garzaya duka Firdausi

12.  Ai dole na jinjina ma wasu
       Wa]anda ke cika aikinsu
       Wa]anda ba sa latti da su
       Nake batu, ku kun san su

13.  Da masu latti da ‘yan fashi
       Da ni da su sam ba bashi
       Babu yabo izuwa sashi
       Na masu ]an banzan fashi

14.  Masu fahimtar darusana
       Allah ya sa ku a Aljanna
       Duk wacce ko ta zamo sauna
       To walla ni babu ruwana

15.   Na so a ce na kira suna
        One-by-one na mutane na
        Amma yawan ku shi ya hana
        Don kar a zo a ji haushina

16.   Don ko hala in mance wata
        Ko ko a ce na zage ta
        Amma ha}i}a ba mafita
        Don wasu kam sai na furta

17.   Irinsu A’isha mai naci
        Na tambaya ba ta sakaci
        Cikin aji ba ta barci
        Tana kiyaye da lokaci

18.   A’isha da ke da Firdausi
        Ai tuni nai muku lasisi
        Yaran da in dai ga nassi
        Ba sa sa~a wa hadisi

19.   Allahu Rabbi ya biya ku
        Ya sa ku aure tamkar ku
        Sannan ya }ara fahimtarku
        Ya yau}a}a muku }arshenku

20.   Kada ki ce na manta ki
        Asma’u yarinyar kirki
        Dukan ajin nan }annenki
        Don kin riga su a gaishe ki

21.   Dake da duk ‘yan }annenki
        Walla kuna nunan kirki
        Amma na kan sha mamaki
        Yadda kike fashin aiki

22.   Khadijah ke ba kya wasa
        Irinki yaya ga Nafisa
        Wacce a yanzun tai nisa
        Wacce a ke ce wa Hafsa

23.   Kada ki manta burinki
        [anki ya zam yaron kirki
        Ya zarce Ibnu Hajar, sonki
        Yai ta wa sunna jan aiki

24.   Ya karya wannan }alubale
        Da tuntuni aka daddale
        Allah ka sa yaron ya }ale
        Kar burin ya bi kwale-kwale

25.   ‘Yar Bilkisu da Jamila
        Har ma na sanya da ‘yar Sala
        Na kan tuno ku da madalla
        Ban so ai maku bulala

26.   Ku daina latti da ke Murja
        [iyar da ba ta da ja-in-ja
        Da Aisha sai kin canja
        Tsawon hijabi }asa ya ja

27.   Dole na sanyo Aishatu
        Da Rabi har da Suwaibatu
        Ko da a yanzun sun ‘yantu
        Sun sauke ba su karatu

28.   Ina kiran ku da alheri
        Allah ya kare dukan sharri
        Ya sa ku auri maza na gari
        Wa]anda basa yin mari

29.   Ina kike Auntie Sadiya
        Ya wacce ba ta jayayya
        Ina tuna ki a zuciya
        Allah yai maki sakayya

30.   In na tuno Auntie Sadiya
        Na kan ji }unci a zuciya
        Allah kai mata sakayya
        Ka ba ta lada na biyayya

31.   Kai mana canjin alheri
        A madadin wanga ha]]ari
        Allah ka }ara mana jari
        Na dangana bisa mu}addari

32.   Rashida yarinyar kirki
        A gai da ke har Antinki
        Ga shawara ta a gare ki
        Ki }ara }wazo gun aiki

33.   Kun ga cikin lissafina
        Dole na sanya da Hassana
        Sannan Nafisa Hasan na tuna
        Mata ga Garba na jinjina

34.   Halima T. Shehu na Kano
        Safiyya ma kan ki zan kwano
        Ke da Faridatu na gano
        Cewa kuna fa da alfano
 
35.   Fatima matar malam ce
        Bintoto mai son darasi ce
        Ki dinga rokon Rabbi ki ce
        Allahu ya sanya ki yi fice 

36.   Na kusa in manta da Sa’a
        Da ke da Safiyya mai sa’a
        ‘Yar Asama kin buga sa’a
        Tun da kina }in masha’a

37.   Dije Lawal }anwata ce
        Da Rabi sun }ulla }awance
        Allah ka sanya kin dace
        Aurenki da hankali kwance

38.   Ke Abu }anwa gun Dije
        Tsaya in ]an yi maki jaje
        Don kan fashi kin cije
        Da ke da Dijale kun saje

39.   Harira na can ]akinta
        Tana biyayya ga mijinta
        Ya Rabbi biya bukatunta
        Ka ninka lada a gareta

40.   Maryamu yaya ga Sakina
        A gai da babbar Antina
        Kanwarki ni ta shiga raina
        Ina ta nuna mata }auna

41.   Ke ko Sakina ki saurara
        Gare ki zan ]an yi ishara
        In dai har ni kika aura
        Wallahi kin tsere asara!

42.   Ya Rabbana na ro}e Ka
        Ka taimaka ma bayinKa
        Wa]anda ke bin manzonKa
        Wanda ya kawo sa}onKa

43.   Ya ‘yan uwana kui hakuri
        Wa]anda ba su cikin tsari
        Wa]anda nam manta, buri
        Na wa}e Daru bila fahari

44.   Ya ]alibaina ku ]an tsaya
        Ga hanzarina guda ]aya
        Don ko karatu za ya tsaya
        Ba na son mu yi jayayya

45.   Ni za na je NYSC
        Don haka dole mu bar darasi
        Kui hakuri kar kui kwafsi
        Duk farko sai yai akasi

46.   Allahu ]alibbai ga su
        Rabbi ka biya bukatunsu
        Ka yafe dukkan laifinsu
        Ka shirya dukkan zuriyarsu

47.   Ka sa su more wa ilimi
        Su dinga aiki da ilimi
        Don ya kasance ko lazimi
        Na zana wanga da al}alami

48.   Ina wa dangi ban kwana
        Ku yafe dukkan laifina
        Mu ro}i Allah duk ya mana
        Sakamakonmu da Aljanna

49.   Ai rabuwa ba ta da da]i
        Bayan sabo da nisha]i
        Mui hakuri har zuwa ba]i
        Mu jure dukkanin ra]a]i

50.   Allah na ke ro}o ya mana
        Falalar gamuwar mu da juna
        Ya sa mu jure da amana
        Da girmamawa gun juna

51.   Ma’assalam ni naka cewa
        Don lokaci na ta }urewa
        Zan ha]a duk nawa-ya-nawa
        In tafi neman dacewa

52.   Shi kenan sai na dawo
        Har tsaraba zan ]an kawo
        Ai baitukan sun ]an yi tsawo
        Amma a nan zan sa tsawo

53.   Nai adu’a a wajen Allah
        Tare da mammatse }walla
        Na ce ya }ara min falala
        Da gafara da yawan sallah

27 ga watan Yuli, 2004

Zariya.

No comments:

Post a Comment