Tuesday, January 11, 2011

WAKEN AKIDAR DAHAWIY

WA{EN A{IDAR [AHAWIY
           
Littafin “Al-Akidatud Dahawiyyah” sananne ne a wajen malamai da ]alibai mabiya Sunnar Annabi tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi. Na koyi karatun litttafin a wajen babban malaminmu Muhammad Auwal Adam wanda aka fi sani da Albani tun wajejen shekarar 1996.

A shimfi]ar karatun malam ya yi bayanai masu jan hankali game da  muhimmancin littafin musamman akan a}idar magabata, ya kuma kawo zantukan malamai wa]anda suka yabi littafin ko suka yi wa ]alibansu wasiyya da cewa su kula da littafin.

Wannan ya sa mini }auna ta musamman ga littafin, abin da ya ja na yi tunanin ya kamata in fassara shi da Hausa. Daga baya kuma na tu}e a kan tunanin cewa ba fassara shi ka]ai zan yi ba, a’a wa}e ya kamata in mai da shi cikin Hausa.

Na yi amfani da karin wa}ar ha]in kan Afirka ta Malam Abubakar Ladan Zariya. Wadda tun ina ]an yaro nake matu}ar sonta.


Malam Abubakar Ladan yana yawan maimaita wani amshi a wa}ar yana cewa:
 
Allah ya Allah ya Allah
Hada kan mu Afirka mu so juna

To ni kuma sai na kan ce duk bayan gunduwa goma:

Allah ya Rabbi abin bauta
                  Kai [ai na ri}a ban shirka ba

Wa}ar tana da layi hur-hudu ne.

Ga ta kamar haka:

1.    Allah Sarki ya mai iko
       Ya Rahman Rabbi ka ban iko
       Allah na kiraya tun farko
       Ba na ro}on wani ba shi ba

2.    Sarki Mahalicci mai kowa
       Ma’abocin girma da uluwwa
       Shi ]ai ya kamata a bauta wa
       Sam bai dace ai shirka ba

3.    Allah yi salati da aminci
       Ga Muhammadu manzon adalci
       Haka alaye masu karamci
       Da sahabbai ni ban ware ba

4.     Wa}ar ga a yau zan rera ta
        Don in bi a}ida na fa]e ta
        Ta [ahawiy yau zan wa}e ta
        Kuma ba larabci zan yi ba

5.     Ro}ona gun Allah Sarki
        Ya yi min baiwar ban mamaki
        Na biya ta a gane ai aiki
        Da a}ida ba yin shirka ba

6.     Dangi ba na son ja-in-ja
        Kun san fa a}ida ce daraja
        In ka ri}e wannan ba danja
        In ba ta ba za ka ji da]i ba

7.     Na za~i [ahawiyya ne ni
        Don na ga tana da mu}ami ni
        Wata ran malam ya hore ni
        Bai bar ni na kauce hanya ba

8.     Ya ce “La yastagni anha
         [alibu ha}}in”  summa alahha
         Har ‘yan yara koda a raha
         A biya masu sam bai ware ba

9.     Shi ne naka so na bi doronta
        Na biya ta da Hausa na wa}eta
        Don yara su haddace manufarta
        Har manya ma ban tsame ba

10.   Baban Jafar mutumin Misra
        Ya yi karatu sannan da kira
        Izuwa hanyar manzon tsira
        Masani ne ba ko na wasa ba

11.   Suka mai sharri suka bata shi
        Suka ce wai ]an shi’a ne shi
        Don ]ai ya ce a bi manzon shi
        Sai yad dage bai zauna ba

12.   Ya rubuta a}ida kuma yac ce
        Wannan shi ne ni na }udurce
        Maganar da suke duka }arya ce
        In ba ta cikin littafin ba
13.   Ita wagga a}ida ta dace
        Don ko ta zam salafiyya ce
        Shi wanga batu an tantance
        Ba zance ne na ]arika ba

14.   Ashabu Rasuli da ogansu
        Duka kan ta su kai addininsu
        Shafi’i, Malik, da na bayansu
        Annu’umanu bai kauce ba

15.   Baban Yusuf  haka Shaibani
        Su ma fa a kan ta su kai ta gini
        Limamin Sunna Shaibani
        [an Hambali ~ai taba shirka ba

16.   Ahlus Sunna sun ha]u kan ta
        Sun koyar sun yi ta sharhinta
        Yanzun ku tsaya zan wa}e ta
        Ba yadda ka san ta da yare ba

17.   Tauhidin da muke cewa mu
        Muka }ulla hakan a cikin ranmu
        Cewa Allah Mahaliccinmu
        {waya daya ne rak ba wai ne ba

18.   Shi bai da abokin tarayya
        Ba mai iya jan Shi da jayayya
        Mun tabbata wanga batu hayya
        Ka bi tauhidi ba shirka ba

19.   Sarki Allah babu kamar Shi
        Ba wani Allah in bayan Shi
        Kowa kake ba ka buwayar Shi
        Bai farko kuma bai }arshe ba

20.   Ba Ya }arewa har abada
        Jujjujayawa sai Ya yarda
        Allah Rayayye ne tun da
        Ba Ya mutuwa bai barci ba

21.   Sam ba a iya a tunano Shi
        Koko ka iya ka fahimce Shi
        Don ba Ya kama da halittunshi
        Shi yay yi halittu ba wai ba

22.    Kuma bai da bukata a wajen su
         Allah shi [ai Ya azurta su
         Ba Ya wahala gun ci da su
         Mai rai Ya kashe bai tsoro ba

23.    Haka zai tashe su dukanninsu
         Bai jin wahala bisa tashin su
         Tun da ma can kafin yin su
         Haka Rabbi ya ke bai canza ba

24.    Su ]in nan ba }ari ne ba
         A cikin mulkinSa da izza ba
         Da dukan siffofi bai kau ba
         Haka nan kuma ba zai canza ba

25.    Ba sai da ya }era halittu ba
         Ya zamo Mahalicci ba haka ba
         Haka ba sai sanda ya tsara ba
         Ya kasance Bariy ba wai ba

26.     Shi Rabbun ne a wajen kowa
          Don shi ya halicci dukan kowa
          Allah Shi ne ke rayawa
          Ba sai da ya }era halittu ba

27.     Ikonsa yana bisa kan kowa
          Haka gun Shi bu}atar ]an kowa
          Shi bai da bu}ata gun kowa
          Sauki komai yake gun Rabba

28.     Huwa Rabbi Sami’un wa Basirun
          Haka Allah laisa ka hu shai’un
          Khalakal Khal}a summa sama’un
          Ba su ~uya ga Allah Sarki ba.

29.    A}dar duka shi yas sanya su
         Haka yats tsaro ajalolinsu
         Ya san aikin da suke yi su
         Tun loton bai yi halittu ba

30.    Ya umurce su su yi ]a’ar Shi
         Haka nan ya hane su su sa~e Shi
         {udurar Allah da mashi’ar Shi
         Bawa ba zai kuwa haura ba

31.    {udurarshi abar zartarwa ce
         Bayinsa gaba daya ni na ce
         Bisa damar Rabbi abar zarce
         Suka juyawa ba su haura ba

32.    Ma sha’a lahun wannan kana
         In ya }i ko to ai ba kana
         Haka Rabbi yake Mahaliccina
         Bai ta~a rauni gun iko ba

33.    Shiryarwa da ~atarwa sai shi
         Falala ga ]ayan adalcin shi
         Ya tsare Yai ma jarabawarshi
         Allah sam bai zalunci ba

34.    Bayi duka kai-kawowarsu 
         Bisa adalcin Mahaliccinsu
         Ko ko falalar wanda ya yi su
         Ba sa wuce wanga mataki ba

35.    Shi bai da sa’a kuma ba tsara
         Ba mai hana aikin da ya tsara
         Ko ture hukuncin da ya tsara
         Yi masa gyara bai taso ba

36.    Ba mai rinjaye a gare Shi
         Duka wannan mu mun ka fa]e shi
         Mun tabbata wanga da aikenShi
         Ba za mu sake mu yi }arya ba

37.    Manzonmu Muhammadu bawan Shi
         Mun tabbata Shi yaz za~e shi
         Ya ri}e shi abin yarda gun Shi
         Bayan shi ba zai wani aike ba

38.    Jagora ne gun manzanni
         Shi ne yak kawo {ur’ani
         Ya zamo }arshen ‘yan sa}onni
         Khalilin Allah ba wai ba

39.    Duk wanda ya zo nan bayan shi
         Yac ce Allah ya aiko shi
         {arya ce ko wane ne shi
         Allah tsine masa ba wai ba

40.    Allah ya aiko manzon Sa
         Izuwa dukannin bayin Sa
         Shiriya yak kawo hasken Sa
         Ya haskaka bai bar zulma ba

41.    {ur’ani zancen Allah ne
         Allah ya saukar wahayi ne
         Kar wanda ya ce Makhlu}i ne
         Bidi’a sam ba kana ce ba

42.    Muminnai sun ce ha}}un ne
         Sun tabbata zancen Allah ne
         Ba ya kama da batu na mutane
         Hakanan yake sam ba tababa

43.    Duk wanda ya ce zancen wani ne
         Wannan tabbas ya zam arne
         Sai ya ci wuta sai ya }one
         Matu}ar bai tuba da sauri ba

44.    Allah ya ce uslihi sa}ar
         Duk wanda ya ce }auli na bashar
         Daga nan muka sam tabbar amsar
         Ba zance ne na halittu ba

45.    Kafirci ne a sifanta shi
         {ur’ani da batun bayin Shi
         Ka kula da batun nan da ka ji shi
         Kauce masa ba tsira ce ba

46.    Wannan zai sa ka yi tsantaini
         Ka wuce arna masu bayani
         Na za}ewa har ya zamo fanni
         Allah da halittu ba ]aya ba

47.    Mun yarda akan ‘yan Aljanna
         Su za su ga Allah har sui murna
         Hakanan {ur’ani yan nuna
         Amma bai ce ga yanayi ba

48.    Ba ma wuce gona da iri mu
         Ba ma cewa da tunaninmu
         Mun sallama imanin kanmu
         Ba mu kutsa ko tababa ba

49.    Wannan ita ce fa a}idarmu
         Tafsirin ba ra’ayoyinmu
         Ingantattun nassoshinmu
         Ba mu yarda da bin son zuci ba

50.    Ba wanda ya tsira a addini
         Sai wanda ya bar biye }aulani
         Ya bi Manzon nan mai {ur’ani
         Ga batun Allah bai ja mai ba

51.    Shubuha ya buge ta ya ]au haske
         {ur’ani kuma yab bi da gaske
         Haka sunnoni duka ban da sake
         Ba tare da bin sambatu ba

52.    Musulunci sam bai daidaita
         Sai taslimi ya }asaita
         Istislami sai ka furta
         Ba neman kaiwa matu}a ba

53.    In ko ka za}e kan ilminka
         Ga abin da haramun ne kanka
         Wannan shi ne zai cuce ka
         Ba zai kuma kai ka ga tsira ba

54.    Wannan bisa shirka zai kai ka
         Ya hana ka fahimtar dininka
         Ya raba ka da ]an imaninka
         Tauhidin ba zai saura ba

55.    Sai dai ka zamo a cikin rikici
         Ka fa]i ka tashi munafurci
         Ba imani ba kafirci
         Kuma kai ba ka ce }arya ne ba

56.    Kai ba ka ce wannan daidai ba
         Ba ka tabbata }aryar zance ba
         Ka sa shakka ba ka huta ba
         Kai ba tsantsar mai saiti ba

57.    Sai waswasi ka zamo ~aidu
         Ba ka a ruwa kai ba ka tudu
         Susa ba ta yiwuwa da gudu
         Ka yi marmaza kai saurin tuba

58.    Duk wanda ya }aryata manzona
         Cewa in an shiga Aljanna
         Za a ga Allah har ai murna
         Ba zai amfana da wannan ba

59.    Ko wanda ya murgu]e nassoshi
         Yai tawili ya bi son ranshi
         Ya guje wa tafarkin manzonshi
         Wannan shi ma ba zai sha ba

60.    Addinin Allah musulunci
         Tawili ko wani ~atanci
         Ba su da }ima sai adalci
         Sai mi}a wuya ba rikici ba

61.    Mai kore sifofin Rabbani
         Wannan ya }aryata {ur’ani
         Hakanan wanda ya ba shi kamanni
         Wannan aiki bai dace ba

62.    Siffofin Allah kyawawa
         Sam ba su kama da sifar bawa
         Sun sha bambam da na ]an kowa
         Wannan haka ne ba tababa

63.    Ya daukaka Allah Mahalicci
         Daga duk wani bawa mabu}aci
         Sarki Allah bai zalunci
         Ka ri}e wannan ka fa]a a gaba

64.    Isra’i mun ce ha}}un ne
         Haka ma Mi’iraji tabbas ne
         Baitul Ma}adis daga nan shi ne
         Yaj je sama ba }arya ce ba

65.    Da jikin shi ya je ba barci ba
         Ba kuma ruhi ban da jiki ba
         Manzonmu ba zai fa]i }arya ba
         Bai na}}asa sa}on Allah ba

66.    Allah ya ]aukaka manzona
         Sallah yab bai wa masoyina
         Allahs sa shi zai ceto na
         In tsira na zam ban ta~e ba

67.    Mun yarda da tafkin da ya ba shi
         Don yas shayar da mutanenshi
         Babu }ishirwa bayan shan shi
         Kuma ]an bidi’a ba zai sha ba

68.    Kofin sha ba zai yi ka]an ba
         Wawa gun sha ba ta taso ba
         Girmanshi ba za ya misilto ba
         Sauran zancen sai an duba

69.    Ceton shi da zai ai tabbas ne
         Shi ne zai ceci mutane
         Wannan zance ne fa sananne
         Tun ba a wajen malammai ba

70.    Allah ya ]au al}awarin Sa
         Kan ‘ya’yan Adam bayinSa
         Cewa su za sui bautar Sa
         Ba za su yi sa~on Allah ba

71.    A’araf aya saba’in da biyu
         Bayan ta ]ari kuma in ya yiwu
         Ka bi sharhi ban da halin gayu
         Kar kai jayayyar ‘yan taba

72.    Adadin ‘yan Aljanna dukansu
         Da wa]anda wuta ce }arshensu
         Allah tuni ya lissafa su
         Ba za ya rage ko }ari ba

73.    Af’alul Khal}i dukanninsu
         Da sanin Sa suke yin aikin su
         Aikin da suke Shi yay yi su
         Ba su da Allah in ba shi ba

74.    Da hukuncin Shi yaw ware su
         ‘Yan aljanna Ya hukunta su
         Haka ‘yan wuta ma Yaw ware su
         Allah kuma bai zalunci ba

75.    Asalin }adara wani sirri ne
         Allah Sarki mai baiwa ne
         Shi ]ai ya sani don gaibi ne
         Ba mai }adara in ba shi ba

76.    Da Mala’ikku, Annabbawa
         Ba wanda yake iya ganewa
         Kuma ba kyau neman kutsawa
         Ba imani ne wannan ba

77.    [ugyani ne da ranshin kunya
         Ka kiyaye kar ka bi ‘yan baya
         Bar waswasi bar zar~a~a~iya
         In ka }i ba za ka falahi ba
 
78.    Allah Sarki ya ]auke shi
         Ilimin }adara daga bayin Shi
         Kuma ya hana nema na sanin shi
         Bai yarda a nemi sani nai ba

79.    La yus’alu amma yaf’alu
         Ayar Allah ce tanzilu
         Haka nan taz zo bisa tartilu
         Ba zance ne na mutane ba

80.    Duk wanda ya ja da hukuncinSa
         Ya }aryata ayar RabbinSa
         Ya kafirce daga dininsa
         Arne ne ba ko musulmi ba
 
81.    Jimlolin nan da na shisshiryo
         Zance ne sam ba wani ~oyo
         Bawa mabu}aci ]an goyo
         Ba zai tsira bila wannan ba

82.    Bayin Allah da waliyyanSa
         Haka nan ulama’u mutanen sa
         Ita sun ka ri}e gun bautar sa
         Ba su }aryata Manzon Allah ba

83.    Nan sun ka tsaya ba su gota ba
         Haddin da a kai ba su keta ba
         Gona da iri ba su zarce ba
         Bautar Allah ba su daina ba

84.    Ilmi ka san fa gida biyu ne
         Na ]ayan su akwai shi sananne ne
         Shi kau na biyun ~oyayye ne
         Allah bai ba bayi shi ba

85.    Imani ba shi da inganci 
         Sai an sa ilmin adalci
         An bar kutse bisa jahilci
         Ba ra’ayin }artin banza ba

86.    Lauhun da {alam mun imani
         Dukkan }adara an yi bayani
         A rubuce ciki mun imani
         Allah ya }adarta ba wai ba

87.    In da bayi za sui gayya
         Don canza abin da ya shisshirya
         {ari da ragi ko jayayya
         Wallahi ba za su iya mai ba

88.    Jaffal }alamu ka ji batuna
         Ma akh]a‘ani bai samu na
         Akasin haka koda ban }auna
         Ba zai kauce ga bari na ba

89.    Bayi ku sani cewa Allah
         Tuni yai tsari shi na jimilla
         Bisa kan hikimar tsarin Allah
         Ba sa haye tsarin Allah ba

90.    Kuma babu ragi haka ba }ari
         Ba canji komai }amari
         Haka cin gyara bar kurari
         Ba za ka iya da Ilahiy ba

91.    Ba mai iya }ara halittunSa
         Koko ya rage masa bayinSa
         Ko da a sama ko nan a }asa
         Wannan fa da]ai ba zai yiwu ba

92.    Wannan a a}ida asali ne
         Ka ri}e shi da kyau ko ka gane
         Don ko maganar {ur’ani ne
         Ba wai maganar bayi ce ba

93.    Ahzab, Fur}an ka karanta su
         Farkon Fur}an sai ka gamsu
         Aya ta biyu an yi batun su
         Harkar }adara ba wasa ba

94.     Ahzab kuwa aya ta talatin
          Da takwas, ka ri}e wannan baitin
          Don na shirya da ba}in Latin
          Ba zai yiwu in ja ayar ba

95.     Allah tsine wa duk wanda
          Yas sa wa Allah andada
          Zai ]an]ana ku]a tai tun da
          Bai zamto mai tauhidi ba

96.     Kutse ba kyau kayin }adara
          Duk wanda ya }i zai yi asara
          Kunya da tsiya da yawan fatara
          Tsira ba zai ta~a samu ba

97.    Zai fa]a ru]u, ta~ewa
         Sai ta aurai ba sa rabuwa
         Zindi}anci zai komawa
         Ba zai zama mai tauhidi ba

98.    Al-arshi da Kursi tabbas ne
         Allah daga su mawadaci ne
         Bayin Allah mabu}ata ne
         Ba za su wadatu da Allah ba

99.     Allah ya kewaye Al-arshi
          Ba ma yarda mu sifanta Shi
          Mun gasgata manzo bawanShi
          Manzon Allah bai }arya ba

100.   Ibrahim ka ga Khalilun ne
          Allah ya ri}e shi ha}i}a ne
          Haka nan Musa ko Kalimun ne
          Ba za mu bi ‘yan ta’a]ili ba

101.   Mun mi}a wuya mun imani
          Mun gasgata ayar {ur’ani
          Ba ma bin duk wani shai]ani
          Ba za mu biye wa son rai ba

102.   Mun yarda da manzannin Allah
          Annabbawa bayin Allah
          Sun kawo addinin Allah
          Ba su tauye sa}on Allah ba

103.   Mun shaida cewa aikinsu
          Wa’azin tauhidin Rabbinsu
          Allah da]a tsira a gare su
          Ko da ]aya ni ban ware ba

104.   Ahlul-}ibla ko musulmi ne
          Matu}ar sun yarda suna a sane
          Cewa manzo jagora ne
          Ba su canza mai addini ba

105.   Ba su }aryata Manzon Allah ba
          Ba su wa sunnanrsa jafa’i ba
          Ba su }etare haddin sunnar ba
          Ba mu kafirtar da musulmai ba

106.   Ba ma rigima kan {ur’ani
          Ba ma sa~i-zarce da mirani
          Ba ma rikici kan addini
          Ba ‘yan tawaye ne mu ba

107.   {ur’ani zancen Allah ne
          Wahayi, Jibirilu amini ne
          Ya kawo sa}on mun gane
          Ba zance ne na mutane ba
  
108.   Ba ma cewa makhlu}i ne
          Maganarmu irin ta sahabbai ne
          Bidi’ar jayayya shirme ne
          Allah bai yarda da wannan ba

109.   Dukkan mai kallon al}ibla
          Don yai sa~on Sarki Allah
          Komai girman sa~on walla
          Ba mu kafirta shi da wannan ba

110.   Sai dai in ya yi giringi]ishi
          Ya }udurce halas ne sa~on Shi
          Wannan ya warware dininshi
          Shi kam bai zam fa musulmi ba

111.   Imani mu ba ma cewa
          Bai inganta ga malaifawa
          Fata na gari ga musulmawa
          Ba mu wa Allah sa~i-zarce ba

112.   Mai kyautata aiki muminni
          Fatan mu garai gun Rahamani
          Ya yi mai rahama ya haye tsani
          Ba mu ce ]an aljanna ne ba

113.   Duk wanda ya sa~a wa Rabba
          Wannan ko muna yi mai tuba
          Istigfari gun ya Rabba
          Ba mu yanke }auna kai nai ba

114.   Ba wanda mu kan ce ya tsira
          Ko ya ta~e ya yi asara
          Kowam mutu ba ma karara
          Ba mu zartar mai da hukunci ba

115.   Yankar }auna da amincewa
          Ka guje, don kar sui ma yawa
          Tsakiyarsu ka zam daidaitawa
          Ba wai ka biye wa guda ]ai ba

116.   Ba ma hana bawa imani
          Don laifi ko don nu}usani
          Sai ya musa tushen imani
          Wannann ba zai ta~a tsira ba

117.   Imani sai ka furta shi
          Can zuci ka ce ha}}un ne shi
          Da ga~arka ka aikata aikinshi
          Malam bai ambaci wannan ba

118.   Dukkan ingantaccen nassi
          Manzo ya fa]a yay yi hadisi
          Mun yarda da su ba tadlisi
          Ba mu mur]e batun manzona ba

119.   Bayin Allah ba fifiko
          Illa ta}awa da yawan tsaiko
          Kan tsoron Allah mai iko
          Ba su nace wa son zuci ba

120.   Muminnai dukka waliyyai ne
          Mafiyinsu yakan ]ara ]a’a ne
          A wajen Allah mai baiwa ne
          Baiwar Allah ba ta }are ba

121.   Mene ne ma’anar imani?
          Ka sakankance kan Rahmani
          Littaffai nai har Manzanni
          Tashin duniya ba gangan ba

122.   {adarori sai ka amshe su
          Ka yarda Ilahi yay yi su
          Alheri, sharri akasin su
          Da Mala’ikku ban manta ba

123.   Wannan fa batun dukkanin shi
          Mun yarda da shi yadda ka ji shi
          Addini ba ma keta shi
          Ba mu gi~are harkar Allah ba

124.   Mun gasgata manzannin Allah
          Ba ma raba addinin Allah
          Duka sun wa’azi kuma sun sallah
          Hanyarsu ba tai bambamci ba

125.   Bayi na cikin al’ummarmu
          In sun zunubi gun Allahnmu
          Wuta za su zuwa, Rabbi tsare mu
          Sai dai ba har abada ne ba

126.   Matu}ar ba shirka suka yi ba
          Ko da ba su bar yin zunubin ba
          Amma ba su bar imani ba
          Ba su kauce wa musulunci ba

127.   Allah ya san ya zai yi da su
          Ko yai rahama ko hora su
          {ur’ani, Mata; surarsu
          Ta nuna hakan ba wai ne ba

128.   Aya ta bakwai bayan forty
          Haka sha shida bayan mi’ati
          Da hadisan baba gun Fati
          Ba zance ne mara hujja ba

129.   Adalci ne ya azabta su
          Rahamarsa ya bar su a cece su
          Ya zuba su a aljanna dukansu
          Allah bai yarda da ~arna ba

130.   Allah na son masu biyar shi
          Su ko arna da ka sa~on shi
          Da wa]anda suke }in ]a’arshi
          Sun ta~e sam ba su dace ba

131.   Allah bai son su yana }in su
          Don sun musa Allah da ya yi su
          Allah ka tsare mu ga aikinsu
          Ka kashe mu ba mui ma shirka ba 
      
132.   Bayan kowa za mui sallah
          In ya mutu za mui mai sallah
          Barrun, fajir bayin Allah
          Matukar bai bar addini ba

133.   Ba ma saka kowa mu a wuta
          Haka aljanna, ba ma wauta
          Shirka in sai shi yaf furta
          Ba mu san sirri na zukata ba

134.   Ba mu yarda a ya}i musulmi ba
          Komai laifi ko ya fi riba
          In ba haddi za ai mai ba
          Ba za a zubar da jini nai ba

135.   Ba ma wa a’imma tawaye
          Ko da sun karkata sun lauye
          Za mui musu ]a’a, ko waye
          Tsine masu ba daidai ne ba

136.   In ba sa~o suka ce ai ba
          Nan kam ba za ai ]a’a ba
          Ba za mu gaza ga du’a’i ba
          [a’arsu ko mu ba mu fasa ba

137.   Addininmu shi ne sunna
          Mu ne jama’ar Ahlus-Sunna
          Ba ma raba kai ba ma kunna
          Sababin sa~ani ba wai ba

138.   In al’amari ba mu gane ba
          Nan take bila wata tababa
          Allah a’alam ba mu nace ba
          Ba mu ce mu mun san komai ba

139.   Shafar huffi addini ne
          Halin tafiya da gida ]ai ne
          Bambamcin na yawan wa’adi ne
          Ba mu }aryata manzon Allah ba

140.   Hajji da jihadi daidai ne
          Zarcewarsu har abada ne
          Jagora ko mai sa~o ne
          Ba zai hana aikin Allah ba

141.   Marubuta mun yarda akwai su
          Gadin aikinmu wazifarsu
          Allah ya girmama harkarsu
          Ba mu }aryata Allah Sarki ba

142.   Malakul-Mauti mun yarda da shi
          [aukar rai shi ne aikinshi
          Azra’ilu wai sunanshi!
          Amma bai tabbata suna ba

143.   Kabari da azaba tabbas ne
          Munkar da Nakir ma mun gane
          Sun zo a cikin nassoshi ne
          Ba mu }aryata nassi ko ]ai ba

144.   Duk ran da }iyama tat tashi
          Kowa sai an gwada kayanshi
          Littafi nai ya karanta shi
          Ba wanda ba zai je gun nan ba

145.   Da sawab da i}ab duk mun yarda
          Ardin aiki ma mun yarda
          Haka nan da Sira]i mun shaida
          Haka Mizani ma ba mu ja ba

146.   Mun yarda da cewa Aljanna
          Da wuta tuni su duka an gina
          Kuma wagga a}ida ta nuna
          Abadan ba za mu yi canji ba

147.   Tun kafin khalkin bashariyya
          Allah yai Janna da Hawiyya
          Yai masu shigan kowacce ]aya
          Allah sam bai ta~a barci ba

148.   Su ‘yan wuta yai musu adalci
          Akasin haka ko ya yi karamci
          Allah ke }addara yin barci
          Allah bai mance komai ba

149.   Samun dama a wajen bawa
          Tare da aikinsa take zowa
          Shi taufi}i baya yiwuwa
          Samun shi ga bawa ba wai ba

150.   Amma samun damar }arfi
          Da wadata su duka sun shafi
          Kafin aikin, ba ma tsafi
          Mu sam ba mu soki hadisi ba

151.   Mun ce bawa, har aikinshi
          Allah Sarki yak }era shi
          Amma bawan yai kasabin shi
          Ba mu karkata mu ga za}ewa ba

152.   Allah ai yai mana sassauci
          Takhlifin Allah ba }unci
          Allah ya san mai ha’inci
          Ba zai wa Allah wayau ba

153.   Don babu dabara gun kowa
          Ko wayau ko kuwa dambarwa
          Allah shi yay isa kan bawa
          Ba zai yi gina daga Allah ba

154.   Hila, harka ba ta yiwuwa
          Gun ]a’a ko kuwa sa~awa
          Sai in Allah ya ba bawa
          Dama, ka ji wannan ba wai ba

155.   Bawa ba }arfi a gare shi
          Sai in Allahu fa ya ba shi
          Sannan ne ai zai same shi
          Wannan ai ba wata tababa

156.   Dukkan harka in ta gudana
          Da mashi’ar Rabbi take nuna
          Ilminshi da }udrar Rabbina
          Da }ada’in Allah ba wai ba

157.   Damar Allah ai tai galaba
          Kan dukka mashi’a ba wai ba
          Haka zartarwar Allah Rabba
          Ta haura dabaru ba wai ba

158.   Allah shi yaf alu ma sha’a
          Kuma ba zalunci a mashi’a
          Ya tsarkaka Rabbi ga yin su’a
          Shi bai dangantu ga ~arna ba

159.   Adu’ar bayin da suke raye
          In sun yi ga wanda suke wa maye
          Za tai amfani, ko waye
          Ba zai iya canza }ada’i ba

160.   Adu’ar Allah ke amsawa
          Da bu}atu shi ke bayarwa
          Shi ke yi wa bawa duka baiwa
          Bawa bai mallaki komai ba

161.   Kuma bai da wadata daga Allah
          Ko da }iftawar bismillah
          Duk wanda ya ce shi zai }ulla
          Yai ridda ba zai ta~a tsira ba

162.   Da gadhab da ridha Allah na yi
          Bisa bayinsa kuma in ya yi
          Ya sha bambam da na mu bayi
          Abadan ba zai zama daidai ba

163.   A a}idarmu da akwai }auna
          Ga sahabban manzo na Madina
          Shi ne Ahmad ]a ga Amina
          Ba mu ware guda muka wurgar ba

164.   Ba ma zamewa gun son su
          Haka ba ma kyara ga ]ayan su
          Ba ma }aunar mai zagin su
          Abadan ba za mu raga mai aba

165.   Sai dai mu kira su da alheri
          {aunarsu akan ta muke fahari
          |atanci gun su mu ce sharri
          Mai yin shi ba zai yi falahi ba

166.   Tabbas }in su ]ugyani ne
          Kafirci ne da jafa’i ne
          Hakanan mun shaida nifa}i ne
          Ba aikin mai tauhidi ba

167.   A a}idarmu ga halifanci
          Bayan manzo mai annabci
          Sai baban A’i ga adalci
          Ijma’i ne ba a sa~a ba

168.   Daga shi kuma sai baban Hafsa
          Sannan Usmanu muna son sa
          Da Aliyyu uba ga tagwawensa
          Sune khulafa ba mu ware ba

169.   A a}idarmu ai mun shaida
          Cewa su ]in ga da]a da shida
          Aljanna su kai, duk an ba da
          Ba wai fa da ka muka shaida ba

170.   Sauran yanzun zan }irgo su
          [alha da Sa’ad da Sa’idunsu
          Da Zubairu, Ubaida amininsu
          AbdurRahman ban ware ba

171.   Duk wanda ya tsarkake harshensa
          Daga zagin matan manzonsa
          Ba ya muzanta sahabbansa
          Wannan bai zam da nifa}i ba

172.   Manyan malumma salafawa
          Da na bayansu bisa kyautawa
          Ahlul-Asari, kuma ‘yan baiwa
          Ba za mu kira su da muni ba   

173.   Fu}aha’u da su mun sanya su
          Mu kullum sai dai mu yabe su
          Ba ma ~atanci a gare su
          Ba mu yarda da mai yin wannan ba

174.   Ba ma cewa mu ga waliyyi
          Ya zarce mataki na nabiyyi
          Sai ma cewa dai da muke yi
          Ba zai kamo wani manzo ba

175.   Mun ce ma annabi }waya ]ai
          Ya zarce waliyyai baki ]ai
          Mun yarda karama gun su da]ai
          Ba mu }aryata manzon Allah ba

176.   Daga nassoshi ingantattu
          Don ba ma aiki da matattu
          A riwaya sai ta amintattu
          Ba mu yarda da zu}i-ta-malle ba

177.   Har yau ka sani a a}idarmu
          Tashi na }iyama zai samu
          Wannan duka sai ya riske mu
          Ba za a yi ba wani bawa ba

178.   Da alamomi duk na }iyama
          Mun imani ba ma }yama
          Rana ma za ta fito yamma
          Rannan ai ba sauran tuba

179.   Sannan Isa ma zai dawo
          Dujal ma zai zo yai yawo
          Hakanan Yajuju su cinye tuwo
          Duka wannan mu ai ba mu ja ba

180.   Amma ba ma gasgata boka
          Ko ]an duba na cikin bukka     
          Ko mai tsafi ba ma shakka
          Cewa ba kan sunna suke ba

181.   Hakanan mai yin da’awar }arya
          Mai sa~awa asalin hanya
          Ta Muhammadu ango na Safiyya
          Aikin ga da]ai ba daidai ba

182.   Sannan fa ha]in kai na Musulmi
          Bisa kan sunna kan Islami
          Wannan daidai ne ba zulumi
          Ba mu yarda da yin sa~ani ba

183.   In an yi ko to dole a tace
          Kan sunna mu kan mun nace
          Ita ce daidai mun tantance
          Ba za mu bi zancen }arti ba

184.   Addinin Allah ai ]aya ne
          Musulunci dole guda ]aya ne
          Sama har }asa ko a ina shi ne
          Sam ba shi da canji ba wai ba

185.   Shi ne addinin manzanni
          Mun san haka ne daga {ur’ani
          Duk mai son }ari na bayani
          Ya wuce gun malam ba ni ba

186.   Musulunci ka ga madaidaici
          Don babu guluwwi, shashanci
          Kuma ba ta}asiri ko baci
          Allah bai yarda da amni ba

187.   Hakanan da iyasi ma ba shi
          Jabari, ta’a]ili ture shi
          {adari, tashbihi mai yin shi
          Da wuya ka ga bai sha kunya ba

188.   Wannan shi ne addininmu
          Fili da a ~oye a}idarmu
          Kuma mun ce mu babu ruwanmu
          Da abin da ka }ara ba mu ba

189.   Sarki Allah mun ro}e ka
          Ka tsare imanin bayinka
          Ka kashe mu akan addininka
          Ba wai mu zamo mun ta~e ba

190.   Ka raba mu da sharrin Shi’anci
          Jahamiyyanci da munafurci
          Hakanan Kadariyya ~atanci
          A gareka ba za mui shirka ba

191.   Da dukan hanyoyi na batattu
          Ba sa bin sunna ba su batu
          Kan gyaran dini, ~a~atu
          Da suke yi ba kan sunna ba

192.   Allah Sarki mai zamani
          Ya wanda ya aiko {ur’ani
          Shi mun ka bi mu mun imani
          Ba za mu biye wa ]agawa ba

193.   Na kawo }arshen wa}ena
          Allah ka cika mani burina
          Lada ya Rabbi ga aikina
          Ya zamo ba don riya ni nai ba

194.   Duk mai son }ari na bayani
          Sharhin Hanafiy zai ji bayani
          Hakanan ko da a cikin matani
          Ba zai rasa sharhi ]ai-]ai ba

195.   Hakanan kuma sharhin Albaniy
          Ya yi shi da kyau ya burge ni
          Ka biye mishi dan ka haye tsani
          Shi jahilci ba riba ba

196.   Na }are wa}ar zan tashi
          Allah sa ba kwa bi na bashi
          Kha]a’in da na yi in kun gan shi
          Gyara shi ba zai ban haushi ba

197.   Ni ne Asgar nai bankwana
          Dangi Allah sa kun amfana
          Don wannan shi ne burina
          Ba wai wa}e ne tsura ba
 
198.   Na sallami kowa zan tashi 
          Allah ya gama mu da manzonShi
          Mu zamo mun sha daga tafkin shi
          Ba wai mu zamo korarru ba

199.   Ya Allah Rabbi ka yafe ni
           Kha]a’i, sahawin da ya faru da ni
           Wa}an nan baiti mi’atani
           Ba }wara ]ai ban gota ba

20 ga watan Janairu, 2003

Zariya

No comments:

Post a Comment