Wednesday, April 6, 2011

TABA KIDI

ABIN MARMARI

Wannan wa}a tana daga cikin wa}o}ina na farko-farko, wa]anda na fara gwada fasahata ta wa}a a kansu.

Asalin abin da ya faru har na yi ta shine, lokacin ina karatu a Legal Misau, wato a tsakanin 1995 kenan zuwa 1997 na kasance mamba a }ungiyar Hausa Fasaha;wadda }ungiya ce ta marubuta da manazartan harshen Hausa. Dukkan ]aliban dake ]aukar darussan Hausa a Kwalejin ‘ya’yan }ungiyarne kai tsaye bisa al’ada.

To amma sai na lura cewa akwai mutane da dama daga cikin ]aliban wa]anda ba su ma so a ce su Hausawa ne ballanta ma a ce suna da wata ala}a ta nesa ko ta kusa da wannan }ungiya, tare da cewa wasunsu ma har da Hausa a cikin darussan da suke nazari a makarantar.

Wannan ya zaburar da ni a kan yin wannan wa}ar don ta zama kamar tunatarwa ga ire-iren wa]annan mutane.

{arin wa}ar na Larabci ne wanda aka fi sani da suna Mutakarib. Yana da kari kamar haka:

Fa-uu-lun  Fa-uu-lun  Fa-uu-lun  Fa-uu-lun
Fa-uu-lun  Fa-uu-lun  Fa-uu-lun  Fa-uu-lun


Ga wa}ar:

1.    Da sunanka sarkin dukan duniya
       Ya Jalla Tabaraka Sarki ]aya

2.    Allahu ka kyautata niyya garan,
       Ka kare ni sharri irin na riya

3.    Ka kare ni sharri da dukkan tsiya
       Ka bani fasahar fa]an gaskiya

4.    Na }are }asidar ga ba gargada
       Na }are da hairan cikin juriya

5.    Salati nake yi da ]imbin yawa
       A gun ]an Amina Balarabiya
6.    Sahabbansa, matansa, danginsa har
       Da sauran wa]anda sukai shiriya

7.    Ina so in nushe mu ya ‘yan uwa
       Zuwa ga muhimmin batun gaskiya

8.    Batun nan nufina akan }ungiya
       Ta Hausa Fasaha idon duniya

9.    A nan tsangayar babu shakka muna
       Da girman isa ba batun fariya

10.  Dukan }ungiyoyi muna kan gaba
       Idan ka yi shakka tsaya ka jiya

11.  Da farko muna da ubanni da ma
       Sauran shugabannin da sun ka tsaya

12.  Suna mana aiki suna ]aukaka
       Batunmu a yau a cikin duniya

13.  Shirinmu shirin raya harshenmu ne
       Muna son ya ]aukaka duk duniya


14.  Ka zauna ka duba ka ]an bincika
       Ka ba ni misalinmu in ka iya

15.  Tsaya in gaya maka ko ka gwada
       Ba za ka iya ba kana shan wuya

16.  Ga kalubale gun students a yau
       Wa]anda a Hausa suke dubiya

17.  Ka gane da cewa kana da haki
       Na ]aukar batun ci gaban }ungiya

18.  Abin kam da kunya a ce wai a yau
       Ana nazarin Hausa nan tsangaya

19.  Amma kuma ba a nufin ci gaba
       Na harshen, ana ta gudun }ungiya

20.  Ku amsa batuna ina tambaya
       Ina manufar raina harshen iya?

21.  A Hausa karin magana an fa]a
       Kowab bar gida ya tsirar da tsiya


22.  A wannan batu dole mui azama
       Muna nazarin Hausa nan Kulliya

23.  Amma mun }iya mun }i mui azama
       Da wannan batu ci gaban }ungiya

24.  Muna soke hanjin cikinmu muna,
       Kirari muna so a ce mun iya

25.  Ha}i}a ina ba mu shawarwari
       Mu so }ungiyarmu mu ]au gaskiya

26.  Mu mi}e mu taru dukan ‘yan uwa
       Mu aikata aikin da }arfin tsiya

27.  Mu lura da cewa dukan }ungiya
       Tana son ta haura mu ko da tsiya

28.  Kirana gareku ku amsa mani
       Ku ciccike forms ]in shiga }ungiya

29.  Muna jin takaicin a ce har a yau
       Wannan }ungiya na ta yin zilliya


30.  Ina kuke ya ‘yan uwa ]alibai
       Da ke nazarin Hausa, zo ku jiya

31.  Ku gane da cewa dukan ci gaba
       Da ma cin ta baya ga ku zai tsaya

32.  Ku san duk abinda ya kai yai kwana
       Na ci gaba ku ne abin godiya

33.  Ku }ara sanin in ko tad dur}ushe
       Ku ne da abin bincike bai ]aya

34.  In zaku tuna wanga harshenmu ne
       Da shi an ka sam mu a Nijeriya

35.  Idan ko hakan ne ina hikima
       Ta janye jiki daga harshen iya?

36.  Ka ba ni dalilinka ko manufa,
       Da tas sa ka ke }in shiga }ungiya

37.  Wannan }ungiya dai ta fanninka ce
       Tana yi da kai kuma ko ka }iya


38.  Abinda kawai ya fi daidai da kai
       Ka ba da hadin kanka baki ]aya

39.  Ina ma nasiha ina garga]i
       Ina sa ka hanya ka san shiriya

40.  Ka mi}a wuya ban da janye jiki
       Ka sa gudumowarka ya ]an iya

41.  Mu harha]a }arfinmu baki ]aya
       Mu tallafi wannan uwar }ungiya

42.  Iyayen azanci suna ta fa]ar
       Wai sarkin yawa na da }arfin tsiya

43.  Allahu ka saka wa ‘yan }ungiya
       Da hairan, ka kare su dukkan tsiya

44.  Da shumagabannin cikin }ungiya
       Da sauran iyayenta baki ]aya

45.  Anan zana huta da wa}ar da nai
       Allah sa mu dace a kan gaskiya


46.  Wa}en nan da nay yi akan }ungiya
       Ta Hausa Fasaha a nan zan tsaya

47.  Sunanta Abin Marmari nai kira
       Cikinta a kan kare harshen iya

48.  Allah yi salati ga Manzo da ma
       Sauran mabiyansa da duk auliya

49.  Ka yafe ni duk zunubaina ka sa
       Wa}en nan ya zamto abin shiriya

50.  Sunana Kabiru Abubakari
       Ina da zama ne a can Zariya

51.  Na rubuta wa}ar a ranar biyar
       Ga watan ga domin bi]ar shiriya

52.  Allah ya ha]a mu a Darussalam
       Ku amsa da amin gaba ki daya

05 ga watan Yuli, 1997

Misau.

TA|A KI[I

Wannan wata wa}a ce da na yi ta don in ambaci wasu mutane da suke nuna mini }auna. Dalilin da ya sa na kiraye ta da wannan sunan shi ne, saboda na yi ta ne a lokuta mabambamta, wato na rubuta mafi yawancin baitocinta ne a lokuta dabam-dabam. Sai daga baya ne na zo na harha]a su suka ba da wa}ar a jumlace.

Karin wa}ar na ]auko shi ne daga wata wa}a da na ta~a gani a wani shiri na wasan Hausa na musamman mai suna Mu shakata.

A wannan shirin wanda firarraki ne ake yi da taurarin wasan Hausa, }ar}ashin jagorancin kamfanin ha]a finafinai na Mandawari ne aka nuno wata shahararriyar jarumar wasan Hausa mai suna Fati Muhammad tana wa}ar bankwana da wasan na Hausa saboda za ta yi aure.

Amma yana da kyau a nan na ambaci cewa na yi wa karin kwaskwarima ko kuma in ce na sake masa salo ta hanyar mai da shi layi biyar biyar; Layin farko gajere ne yayin da ukun tsakiya suke da tsayi iri guda, sai kuma layin }arshe wanda shi kuma ya fi sauran tsayi.

Wa}ar tana da amshi kamar haka:

          Ya Tabara,
          Ya Rabbi ka ba mu tsira da dacewa

Maimakon cewa da take yi:
        
         Ya Muhammad,
         Sunnarka nake ta so in ta ya]awa

Ga wa}an nan:

1.    Ya Tabara
       Rabbana ka da]an basira
       Baitukan nan duk na tsara
       Ka tsare ni ga yin asara
       Har na }are ni na zam ba ni sarewa


2.    Gun Rasulu
       Nai salati gun Khalilu
       Rabbi Sarki Zul Jalalu
       Dukka rana har da lailu
       Shi nake ro}o ya yi mani dacewa

3.    Wanga baiti
       Nai yabo gun Alu-Baiti
       Har sahabbai masu saiti
       Ko da Manzo yai wafati
       Sunnarsa suke ta bi har da ya]awa

4.    Wagga wa}a
       Rabbi }ara min haza}a
       Baitukana duk na sa}a
       Rabbi ro}ona na mi}a
       Laifukan da nake da su kai ta yafewa

5.    Baitukana
       Wanda yau su zani gina
       Zuciyata babu }una
       Don masoya za ni nuna
       Ni Kabiru ina da su ba su }arewa


6.    Nura Tela
       Gwarzo angon Nabila
       Za mu }ara ma da Laila
       Wata yarinya jamila!
       Su biyun duka sai ka zam za ka aurewa

7.    Mai gidana
       Ni gareka ina ta }auna
       Alheri ne batuna
       Sai ka yafe kurakuraina
       Don ko Rabbi yana ta son masu yafewa


8.    Mai jama’a
       Kai ka koya min sana’a
       Ka ga ni dai na yi sa’a
       Walla ni ba na bara’a
      Gun yabo ko ka ga ni ba ni sarewa

9.    Zo ka zauna
       Kai Mu’awiya ]an uwana
       [an tsaya ka ji baitukana
       Yaushe za mu wuce Kaduna
       Ran bukinka Kaduna can za mu tarewa!

10.   [an Barewa
        In kana can mui ta kewa
        Mui ta burin }arikewa
        In ka dawo babu yawa
        Allah sa NECO gaba ]ai ka cinyewa

11.   Sai gareka
        Kai Aliyyu ina yabon ka
        Na amince ba ni shakka
        Kanka, ba rowa gare ka
        Allah sa Hauwa’u kai za ka aurewa

12.   Ni uwata
        Ba ni daina yabo gareta
        Don tana sona, batunta
        Duk a kwanan rayuwarta
        Addu’a taka yi gareni da dacewa

13.   Har da Abba
        Abbana na da haiba
        Addu’a naka yi ga Abba
        Ya Ummi da ke da Abba
        Allah sa Aljanna ku za ku komawa


14.   [alibaina
        Duk cikarsu suna ta so na
        Addu’ar kirki a kaina
        Gun Tabaraka Khaliqina
        Shi suke ro}o da]ai ba su fasawa

15.   Zaina Abu
       Ya mai kyau babu aibu
       Ni ro}o na ga Rabbu
       Shi ne Masani na gaibu
       Ni ya }addara Abu ke za ni aurewa

16.   Sai gare ki
        Rabi Asgar na yabon ki
        Babu shakka kin yi aiki
        Lada Allah ya ba ki
        Allah sa ladan zumunci ki kwashewa

17.   Na waiwayo ki
        Ke Suwaiba kina da kirki
        Na jinjina wanga aiki
        Ni na yaba taimakonki
        Allah sa Firdausi ke za ki zarcewa


18.   Har da kai ma
        Khamis ya ba da himma
        {aunarmu yake da zimma
        Allahu ya }ara himma
        Gun ibada don ka zam ba ka ta~ewa

19.   In na juyo
        Gun Amini babu ~oyo
        Zan yabo gun masu wayo
        Kai Ahijjo ka daina wayyo
        Rabbana zai taimake ka da dacewa

20.   Auwaluna
        Mai Shago zo ka zauna
        Na jinjina jarumina
        Malami kuma sahibina
        Gun hadisi ni da shi naka togewa

21.   Ka ga Nura
        Shi aboki ne na fira
        Mai haza}a ne da lura
        Allah sa duka za mu tsira
        Ran }iyama duk sira]i mu haurewa


22.   Masu niyya
        Jarumi angon Badiyya
        ‘Yar mutunci ce da kunya
        Ga ta ‘ya ce mai biyayya
        Kai abokina fa ya sami dacewa

23.   Jarumina
        Albani malamina
        Kai nasiha nan gurina
        Allah saka ma da Janna
        Allah kar~a ayyukanka da sakawa

24.   Sannu Gamji
        Murtalan sunna da caji
        Ko gida  ko da a daji
        Ba ni shakka kanka ban ji
        Ayyukan da kake na hairan da kyawawa

25.   Allah saka
        ‘Yan uwa kun ba ni fuska
        Kun bi Allah babu shakka
        Ku zumunci kun ha~akka
        Rabbi yai baiwa gareku da sakawa


26.   Ya masoya
        Gaisuwa naka yi masoya
        Nan nake so za na juya
        Zuciyata ba }iyayya
        Sai batun }auna gareku da godewa

07 Ga watan Janairu, 1999

Zariya



1 comment:

  1. Rabbana "Malam" tsare Shi ## Hassadar makiya a kan Shi
    Kai dadin hikima gare Shi ## Har basira duk ka ba shi
    Yai ta ci gaba babu fashi

    Dalibin ku:
    Muhammad

    ReplyDelete